Menu

Zabura 137

BIB

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.

2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,

3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”

4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?

5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.

6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.

7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”

8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,

9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

Everything we make is available for free because of a generous community of supporters.

Donate