Menu

Zabura 129

BIB

1 Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,

2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.

3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.

4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya ’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.

5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.

6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;

7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.

8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”

Everything we make is available for free because of a generous community of supporters.

Donate